GAJERAN LABARI, Kano Ayau Hausa

Kotu ta yi watsi da karar Walter Onnoghen

Kotun daukaka kara ta Najeriya ta yi watsi da bukatar da dakataccen alkalin alkalan kasar Walter Onnoghen ya gabatar ta neman kotun da’ar ma’aikan kasar ta dakatar da shari’arsa wadda gwamnatin Najeriya ta shigar.

A hukuncin da ta yanke ranar Laraba, kotun ta yi watsi da bukatar ce domin ba a gabatar da dalilan sauraron karar ba kamar yadda dokokin shari’a suka tanada.

Hukuncin na nufin alkalin alkalan zai ci gaba da fuskantar tuhuma a gaban kotun da’ar ma’aikatan, wadda ta dage zamanta domin dakon sakamakon karar da Mr Onnoghen ya daukaka.

Shugaba Buhari ya dakatar da Mista Onnoghen ne bisa shawarar kotun da’ar ma’aikata wacce ta samu alkalin alkalan da laifin kin bayyana cikakkun kaddarorinsa lokacin da aka nada shi kan mukamin a 2017.

Sai dai Mista Onnoghen ya ce ba da gangan ya yi hakan ba, yana mai cewa mantawa ya yi.

Hakan dai na zuwa ne kwana daya bayan majalisar shari’a ta kasar ta bai wa alkalin alkalan da aka dakatar da sabon mukaddashin da aka rantsar Mohammed Tanko Ibrahim wa’adin mako guda da su mayar da martani kan korafe-korafen da aka shigar gabanta.

Leave a Reply