Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Dokta Rabi’u Musa Kwankwaso ya yi kira ga ‘yan Najeriya su zabi Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Alhaji Atiku Abubakar a zaben 2019 domin shi ne zai magance yunwa.
Kwankwaso ya bayyna haka ne a lokacin kaddamar yakin zaben shugaban kasa na Jam’iyyar PDP a Jihar Sakkwato.
Kwankwaso ya tabbatar da cewa Atiku Abubakar shi ne wanda zai inganta harkokin ilmi tare da samar da hanyoyi da kuma asibitoci masu inganci a fadin Nijeriya.
Har wa yau Kwankwaso ya bukaci al’ummar Nijeriya maza da mata su marawa Atiku baya domin zai habaka harkokin noma da kuma taimakon al’umma.