Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya, ASUU ta sake tsawaita yajin aikin da take ciki.
ASUU ta yanke wannan shawarar ce bayan zaman Majalisar Kolinta a daren jiya, inda ta ce za ta cigaba da yajin aikin har sai an samu maslaha.
Idan ba a manta ba, a watan Fabrairu ne aka fara yajin aikin na gargadi, sannan ta tsunduma na sai baba-ta-gani a watan Maris.
Kimanin wata shida ke nan yanzu ana yajin aikin.