Kano Ayau Hausa, WASANNI

Ronaldo zai buga wa Newcastle Champions League

Dan wasan Portugal, Cristiano Ronaldo zai zo kungiyar Newcastle idan kungiyar ta samu shiga Gasar Zakarun Turai ta badi.

Haka na kunshe ne a cikin yarjejeniyar da dan wasan ya sa hannu da Kungiyar Al Nassr ta Saudiyya, wadda take da alaka da kungiyar ta Newcastle ta Ingila.

Ronaldo dai ya sauka a Birnin Riyadh domin fara wasa da sabuwar kungiyarsa, inda zai kasance dan kwallo mafi daraja a duniya.

A wani bangaren kuma, akwai alama Ronaldo din zai sake haduwa da Sergio Ramos da Luka Modric a kungiyar ta Newcastle a gasar ta badi, domin kungiyar ta fara zawarcin ’yan wasan guda biyu.

 

Leave a Reply