BABBAN BANGO, Kano Ayau Hausa

‘Kwankwaso zai samu kuri’a miliyan 12 a Arewa’

Tsohon dan majalisar wakilai, mai wakiltar Kiru da Bebeji a Jihar Kano, Abdulmumin Jibrin Kofa, ya ce Sanata Rabi’u Kwankwaso, ɗan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, yanzu shi ne zai gaji ɗaukacin ƙuri’un da ƴan arewa ke kaɗa wa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a zaɓe.

Jibrin ya bayyana haka ne a jiya Juma’a, a wata hira da gidan talabijin na Channels da Daily Nigerian Hausa ta kalato.

Idan dai za a iya tunawa, an yi ta raɗe-radin cewa Kwankwaso zai nemi magoya bayansa su zaɓi Bola Tinubu, ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023.

Da yake mayar da martani kan wannan batu, Jibrin, wanda shine kakakin yakin neman zaben shugaban kasa na Kwankwaso, ya ce tsohon gwamnan baya tunanin haɗewa da APC.

Ya ce babu wani ɗan takarar shugaban ƙasa da zai samu kuri’u fiye da Kwankwaso a yankin Arewacin kasar nan.

“Mun karyata wadannan karairayi da ake ta yaɗa wa akai-akai. Wani yunƙuri ne na ba wa jama’a ra’ayi da bai dace ba don wata ƙungiya ko biyu su sami damar ɗaga matsayinsu a bainar jama’a,” inji shi.

“Kwankwaso gogaggen ɗan siyasa ne. Mu da gaske mu ke. Ba dan wani mu ke takarar nan ba kuma na sha fadar haka a lokuta da dama.

“Sabo da haka ina kira ga al’umma da su yi watsi da wannan farfaganda cewa Kwankwaso na yi wa Asiwaju aiki ne ko za mu haɗe da APC .

“Ya za ai ma haka ta yiwu. Mutumin da shi ne ke da ikon Arewa gaba ɗaya. Mutumin da shi zai gaji ƙuri’u miliyan 12 na Buhari a Arewa. Kwankwaso ya fi ko wanne ɗan takara farin jini da masoya da mabiya a halin yanzu,” in ji Kofa.

Leave a Reply