Wannan na zuwa ne bayan daukaka kara da tsagin tsohon Gwamnan Jihar, Ibrahim Shekarau ya yi na neman ta ayyana Haruna Danzago a matsayin shugaban jam’iyyar APC na jihar.
Haka nan, Kotun Kolin ta ce hukuncin da ta yanke ya shafi sauran kararraki biyun da aka daukaka a shari’ar.
Kamar yadda muka kalato daga Aminiya.
Idan dai za a iya tunawa, Kotun Daukaka Kara ta kori kararraki ukun da aka gabatar mata a Fabrairun da ya gabata saboda rashin cika sharudda wajen shigar da kararrakin, tare da cewa matsalar ce ta cikin gida ce wadda ba sai an fita waje don magance ta ba