GAJERAN LABARI, Kano Ayau Hausa

Kashe Ummita: Kotu ta tura Dan China gidan yari

Rundunar yan sandan jihar Kano ta gurfanar da ɗan Chinan da ake zargi da kisan Ummukulsum Sani Buhari, wadda aka fi sani da Ummita a ranar Laraba, gaban wata kotun majistire.

Ana zargin Mista Geng Quanrong da kisan matashiyar, lamarin da ya ci karo da sashe na 221 na kundin laifuka na jihar Kano, a cewar kotun.

BBC Hausa ta ruwaito kotun a ta aike da dan kasar Chinan kurkuku.

Lamarin ya faru ne ranar Juma’a da dare, inda Geng Quanrong, mai shekara 47, ya kutsa kai gidansu Ummita a unguwar Kabuga cikin karamar hukumar Gwale.

Kisan Ummita ya tada hankalin al’umma ‘r jihar Kano da dama har da Najeriya, abinda ya jawo mutane suka dinga neman ayi mata adalci a kafafen sada zumunta.

Leave a Reply