Gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya Umarci duk Wani Dake Rike da Mukamin Siyasa a Gwamnatin sa kuma yake son Takara daya aje aikinsa daga yanzu zuwa Litinin 18 ga Watan da muke ciki.
Cikin wata Sanarwa mai dauke dasa hannun Daraktan Yada Labaran Gwamna, Malam Abba Anwar yace Hakan ha zama wajibi duba da tanade tanaden Sashi na 84 (12) cikin Baka na Sabuwar Dokar Zabe.