Kano Ayau Hausa, Manyan Labarai

An kashe shugaban ‘yan ta’addan duniya

Amurka ta sanar cewa sojojinta sun hallaka jagoran kungiyar Al-Ka’ida, Aiman Al-Zawahiri a wani hari a kasar Afghanistan.

Shugaban Kasar Amurka, Joe Biden ya ce an kashe Al-Zawahiri ne ta hanyar harin jirgi mara matuki.

“Yanzu an yi hukunci na adalci, an kawar da jagoran ’yan ta’addan daga doron kasa,” inji Biden, a lokacin da yake tabbatar da rahoton kashe Aiman Al-Zawahiri a ranar Litinin.

Jagoran na Al-Ka’ida yana daga cikin mutanen da gwamnatin Amurka ke zargi da kitsa harin ranar 11 ga Satumbar 2001, wanda ya yi wa kasar mummunar illa.

Kudin jirgin sama daga Abuja zuwa Kano Naira 135,000

Biden ya ce kashe Al-Zawahiri zai “zai sanyaya zukatan” iyalan mutanen da harin 11 ga Satumbar 2001 ta shafa.

Al-Zawahiri mai shekara 71, shi ne jagoran Al-Ka’ida tun daga shekarar 2011 bayan an kashe wanda ya asasa kungiyar, Osama bin Laden, a kasar Pakistan.

Kawo yanzu dai kungiyar Al-Ka’ida ko gwamnatin Taliban da ke jagorantar kasar Afghanistan ba su ce komai ba gane da ikirarin na Mista Biden.

Leave a Reply