Kano Ayau Hausa

An kashe jagororin ‘yan bindiga a Zamfara

Jaridar PRNigeria ta ruwaito cewa sojojin sama na Najeriya sun samu nasarar hallaka wasu ƙasurguman ƴan fashin daji waɗanda ke addabar ƙauyukan jihar Zamfara.

Rahoton ya ce an samu nasarar kashe ƴan fashin ne a wasu hare-hare da jiragen sojojin Najeriya suka kai a wasu ƙauyukan jihar Kaduna.

Waɗanda aka kashen a cewar rahoton sun haɗa da Jibrin Gurgu, da Isah Jauro da kuma wani da ake kira Tambuwal.

Sauran sun haɗa da Noti, da Bala, da Yunusa da kuma Burti.

Bayanin da jaridar ta samo ya ce an kai farmakin ne a wasu sabbin sansanonin ƴan fashin a yankin ƙaramar hukumar Giwa da ke jihar Kaduna.

Haka nan an kai wasu hare-haren a yankunan ƙananan hukumomin Igabi da Birnin Gwari.

Wata majiyar tsaro ta ce an ga dacewar kai harin ne bayan rahotannin da ke cewa an samu ƙaruwar ayyukan ƴan bindiga a yankin.

Leave a Reply