BABBAN BANGO, Kano Ayau Hausa

Sojojin Najeriya sun sake gano ‘yan matan Chibok biyu da ‘ya’yansu

Bataliya ta 202 ta rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta sun sake kubutar da wasu ‘yan matan Sakandiren Chibok guda biyu a jihar Borno.

Dakarun na Najeriya sun ce ‘yan matan biyu tare da ‘yayansu na asibitin soji inda ake duba lafiyarsu.

A wani sako da Sojojin suka wallafa a shafinsu na Tuwita sun ce sun ceto mata hudu ciki har da ‘yan matan Chibok biyu a lokacin wani samame da suka kaddamar

Sama da ‘yan matan Sakandiren Chibok 200 ne dai mayakan Boko Haram suka sace a shekarar 2014

To amma an kubutar da dama da cikinsu, sai dai har yanzu wasu na hannun mayakan na Boko Haram, kamar yadda BBC ta ruwaito.

Leave a Reply