BABBAN BANGO, Kano Ayau Hausa

Sarkin Zurmi da aka dakatar ya rasu

Sarkin Zurmi, na Jihar Zamfara Alhaji Abubakar Atiku da aka tsige kwanakin baya ya rasu.
Sarkin ya rasu ne a Dubai bayan fama da matsanancin rashin lafiya.
Idan ba a manta ba, a 27 ga Afrilu ne Gwamnan Jihar Zamfara, Muhammad Bello Matawalle ya dakatar da sarkin bisa zarginsa da taimakon harkokin ta’addanci a jihar.

Sarkin ya rasu ne a ranar Lahadi, kuma tuni aka fara shirye-shiryen dawo da gawarsa domin mata sutura.

Leave a Reply