Jami’ai a Amurka suna ce tsananin hunturu da ke ratsa arewacin Amurka na ci gaba da sanadin mutuwar mutane a jihar New York da ke Amurka.
Shugaban gundumar Erie Mark Poloncarz ya ce akalla mutum 34 ne suka mutu a gundumar ciki har da birnin Buffalo.
Tsananin sanyi tare da dusar ƙanƙara da ke sauka a faɗin Amurka tun lokacin hutun Kirsimeti a ƙarshen makon da ya gabata ya yi sandin mutuwar akalla mutum 60 a jihohin ƙasar takwas, kamar yadda muka ruwaito.
Gundumar Erie ce aka fi samun yawan waɗanda suka mutu a ‘yan kwanakin nan.
To amma an fara samun sauƙin yanayin a wasu jihohin ƙasar ciki har da New York