Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nada sababbin ministoci domin maye gurbin wadanda suka sauka da wadanda ya sauke daga kan mukamansu.
Shugaban majalisar dattawan Najeriya Sanata Ahmed Lawan ne ya karanto sunayen sababbin ministocin da Shugaba Buhari ya aike wa majalisar a zaman da ta yi ranar Talata.
Wadanda aka tura su ne: Umana Okon Umana (Akwa Ibom), Henry Ikechukwu Iko (Abia State), Ademola Adegoroye (Ondo state), Odum Odi (Rivers State), Goodluck Nnana Opia (Imo State), Umar Ibrahim El-Yakub (Kano State) and Joseph Ukama (Ebonyi State).