Rundunar ‘yan sanda a jihar Nasarawa da ke ta ce ta gano gidan da ake zargin sayar da jarirai a karamar hukumar Karu ta jihar.
BBC Hausa ta rawaito cewa rundunar ta ce ta ceto mata shida da kuma jariri ɗan wata shida a gidan.
A sanarwar da ya fitar, jami’in hulda da jama’a na yansandan jihar, DSP Ramhan Nansel ya ce da misalin 2 na rana su ka kai samame Karu bayan samun wasu bayanan sirri, kamar yadda muka kalato daga Daily Nigerian Hausa.
Ya ce ana basaja da gidan ne a matsayin gidan kula da marayu. Sai dai bincike ya gano cewa ana garkuwa da kananan yara ana yi musu ciki sannan a sayar da jariran da suka haifa.
An dai cafke wasu mutum uku da ake zargin ke aikata wannan muggun aika-aika.