Labarai

Allah Ya yi wa Birgediya Abba Kyari rasuwa

Allah Ya yi wa tsohon Gwamnan Arewa ta Tsakiya Birgediya Abba Kyara rasuwa bayan ya yi fama da jinya, inda ya rasu yana da shekara 80 a duniya.
Shi dai Abba Kyari ya zama gwamnan Arewa ta tsakiya ne a zamanin mulkin tsohon shugaban kasa na mulkin Soja, janar Yakubu Gowon, daga ranar 28 ga watan Mayu zuwa watan Yuli na shekarar 1975. A shekarar 1967 ne janar Yakubu Gowon ya samar da jihohi goma sha biyu a Najeriya bayan ya rushe shiyyoyin Arewa da na Kudancin Najeriya, inda a cikin shiyya Arewa kadai sai daya samar da jihohi guda shida, daga cikinsu akwai jahar Arewa ta tsakiya, wanda daga bisani aka canja mata suna zuwa Kaduna a shekarar 1976. Abba Kyari ya gaji tsohon gwamnan Arewa, Birgediya Hassan Usman Katsina, yadda abin ya faru kuwa shine a shekarar 1966 wasu kananan Sojoji yan kabilar Ibo suka yi juyin mulki ta hanyar kashe Sardauna Tafawa Balewa, shugaban shiyyar yammacin Najeriya da kuma sauran manyan Sojoji yan Arewa.

Leave a Reply