WA'AZIN KIRISTA

Muhimmancin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara

Muhimmancin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara

Wurin Karatu: Matta 1:21-23 :–

“Za ta haifi da; kuma za ka kira sunansa Yesu; gama shi ne za ya ceci mutanensa daga zunubansu. Dukan wannan fa ya zama domin a cika a in da Ubangiji ya fadi ta baki annabi, cewa, duba, budurwa za ta yi juna biyu, za ta haifi da, za a kira sunansa Immanuel; watau, Allah tare da mu.”

Waxannan ayoyin, cikon annabcin Annabawa akan zuwa Yesu Almasihu domin ceto masu zunubi.

Littafi Maitsarki na tabbatar mana kyawawan sunayen Yesu masu ma’ana kamar haka;

  1. Yesu – Gama shi ne za ya ceci mutanensa daga zunubansu.
  2. Immanuel – Watau, Allah tare da mu.

Da ma’anar sunayen Yesu masu girma da daraja, muna iya san Mahimmancin Krisimas tare da dallilin Allah Ubangiji Allah ya aiko shi a duniya.

A takaice ga Mahimmancin Krisimas:

  1. Domin a tabatar da kamnar Allah Ubangiji ga dukan duniya ko ga Bil Adama baicin zunubin su. Watau Allah ya aiko da Yesu Almasihu a duniya domin Allah na kamnar duniya ne (Yohanna 3:16).
  2. Domin Kiristoci su tabbatar wa duniya kamnar Allah ta wurin Yesu Almasihu.
  3. Krisimas shaida ne cewa Yesu Almasihu ya zo duniya domin ceton duniya.
  4. Mahimmancin Krisimas domin a kyautata zamantakewa
  5. Mahimmancin Krisimas shi ne kara dankon zumunci da karfafa juna a cikin bangaskiya.
  6. Domin girmama da daraja Yesu Almasihu.
  7. Krisimas wata shaida ne fa da cewa ceto ta shigo duniya
  8. Mahimmancin Krisimas shi ne salama ta shigo duniya.
  9. Mahimmancin Krisimas domin sasanci tsakanin mutum da Allah da kuma sasanci ne tsakanin mutum da mutum.
  10. Mahimmancin Krisimas na tattare alherin Ubangiji Allah ga Bil Adama.
  11. Mahimmancin Krisimas domin shaidan Bishara salama fa ceto.

Leave a Reply